Take a fresh look at your lifestyle.

SHUGABA BUHARI YA GAYYACI GWAMNAN IMO, MINISTAN MAKAMASHI

0 186

Shugaban Najeriya  Muhammadu Buhari ya gayyato Gwamnan Jihar Imo  Hope Uzodinma ,Ministan makamashi, Abubakar Aliyu, da Babban mai bada shawara akan tattalin arziki, Farfesa Doyin Salami, domin gana wa da Shugaban kasa a fadar shi dake Abuja .

Tattaunawar ta kasance ne akan halin  da Jihar Imo ke ciki,da kuma halin da harkokin samar da wutar lantarki da tattalin arziki suke ciki

Za’a iya tunawa shugaban kasa yayi tir da rikici da lalata kayayyaki da rusa gidaje har da samar kayan ‘Yan sanda da  gidan  shugaban kungiyar Ohaneze Ndigbo farfesa George Obiozor, kuma yayi alkawarin sake duba halin tsaro a kudu maso gabashin Najeriya..

Hakazalika Shugaba Buhari ya nuna rashin jin dadin shi game da irin halin karancin hasken wutar lantarki da yaki ci yake cinyewa,ya baiwa ‘yan  Najeriya hakuri tare da alkawarta shawo kan matsalar.

LADAN  NASIDI

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *