Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya koma Abuja bayan ya shafe sama da makonni biyu a garin Daura na jihar Katsina.
Shugaban ya samu tarba ne a bangaren shugaban kasa na filin jirgin saman Nnamdi Azikiwe da ke Abuja a yammacin ranar Litinin da ta gabata ta hannun shugaban ma’aikatan fadar sa, Farfesa. Ibrahim Gambari da Ministan Babban Birnin Tarayya, Mohammed Bello.
![]()

![]()
Shugaban na Najeriya ya kwashe sama da makonni biyu a garin Daura, inda ya bar Abuja ranar 23 ga watan Fabrairu domin halartar zaben shugaban kasa da aka gudanar a ranar 25 ga watan Fabrairu.
Ana sa ran zai koma cikin mako guda don kada kuri’arsa a zaben gwamna, wanda aka shirya yi a ranar Asabar 18 ga Maris 2023.
Leave a Reply