Take a fresh look at your lifestyle.

Wasu karin ‘yan Najeriya 107 sun dawo daga kasar Libya

0 154

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta NEMA, ta sake karbar wasu ‘yan Najeriya 107 da suka makale a birnin Tripoli na kasar Libya.

 

Hukumar ta bayyana hakan ne a wata sanarwa da ta fitar ranar Laraba a Legas.

 

Hukumar NEMA ta ce wadanda suka dawo sun isa filin jirgin saman Murtala Muhammad, Cargo Wing, Ikeja, da yammacin ranar Talata a cikin jirgin Al Buraq Air Boeing 737-800 mai lamba 5A-DMG.

https://von.gov.ng/107-more-nigerians-return-from-libya/

Wadanda aka dawo da su sun hada da maza 53, mata 52 da jarirai biyu.

 

Darakta Janar na NEMA, Mista Mustapha Ahmed ne ya karbi bakuncin wadanda suka dawo a madadin gwamnatin tarayya a hukumance.

 

Kungiyar kula da ‘yan gudun hijira ta duniya tare da goyon bayan abokan hulda na kasa da kasa, tana taimakawa ‘yan Najeriya da ke makale a Libya domin komawa gida tun shekarar 2017.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *