Take a fresh look at your lifestyle.

Kotu Ta Kori Alex Otti A Matsayin Zababben Gwamnan Jihar Abia

0 93

Wata babbar kotun tarayya da ke zamanta a jihar Kano ta soke takarar zababben gwamnan jihar Abia, Dr Alex Otti.

 

 

Kotun da ke karkashin Mai shari’a M N Yunusa ta kuma soke takarar duk wasu masu rike da tutar jam’iyyar Labour a jihohin Abia da Kano.

 

 

KU KARANTA KUMA: Alex Otti ya lashe zaben gwamnan jihar Abia

 

 

Yunusa ya yanke hukuncin cewa fitowar su bai dace da tanadin dokar zabe ta 2022 ba.

 

 

Alkalin ya yanke hukuncin ne a kan karar mai lamba FHC/KN/CS/107/2023 da wani Mista Ibrahim Haruna Ibrahim ya shigar a kan jam’iyyar Labour da kuma hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa.

 

 

KU KARANTA: An yi murna a jihar Abia yayin da Alex Otti ya zama zababben gwamnan jihar

 

 

“Jam’iyyar da ba ta bi tanade-tanaden dokar zabe ba, ba za a ce tana da dan takara a zabe kuma ba za a iya bayyana ta a matsayin wadda ta lashe zabe ba; saboda haka, kuri’un da aka baiwa wanda ake kara na 1, kuri’a ce ta bata,” inji alkalin.

 

 

L.N

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *