Hukumar binciken tsaron Najeriya ta ce ta fara gudanar da bincike kan hatsarin da wani jirgin sama kirar Jabiru J430 da ya yi hadari a unguwar Ikeja da ke jihar Legas a ranar Talata.
Jirgin mai haske mai lamba 5N-CCQ.ya yi hadari kuma ya fashe da wuta a lokacin da yake cikin wani jirgin gwaji bayan karfe 1500 (1400hrs GMT).
NSIB COMMENCES INVESTIGATION INTO AN ACCIDENT INVOLVING A JABIRU J430 AIRCRAFT IN LAGOS
The Nigerian Safety Investigation Bureau (NSIB) has been notified and commenced investigation into an accident involving a Jabiru J430, a light single airplane with Nationality pic.twitter.com/1bbxRgJTVs
— Nigerian Safety Investigation Bureau (@nsib_nigeria) August 1, 2023
Ofishin ya ce jirgin na kamfanin Air First Hospitality & Tours ne kuma yana dauke da fasinjoji biyu kafin ya fadi a kusa da Oba Akran, wani wuri mai cunkoso a Legas. Babu mace-mace.
Da yake tofa albarkacin bakinsa kan lamarin, kakakin hukumar bayar da agajin gaggawa ta kasa NEMA a jihar Legas, Ibrahim Farinloye ya tabbatar da cewa an ceto mutane biyu da ke cikin jirgin da ransu.
Today, at the location of the crash, I expressed my appreciation of their commendable efforts to the first responders and residents who actively participated in the rescue operation.
The incident involved a single engine fixed-wing Jabiru aircraft with registration number 5NCCQ… pic.twitter.com/fPsccaKdIi
— Babajide Sanwo-Olu (@jidesanwoolu) August 1, 2023
A yammacin ranar Talata ne Gwamna Babajide Sanwo-Olu na jihar Legas ya ziyarci wurin da hatsarin ya afku a Ikeja inda ya yabawa wadanda suka kai daukin gaggawa da mazauna yankin da suka shiga aikin ceto.
Ladan Nasidi.
Leave a Reply