Take a fresh look at your lifestyle.

Masu Rijistar Zabe 32,000 Suka Karbi Katinan Su A Jihar Legas

Aisha Yahaya, Lagos

0 283

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa, (INEC) ta ce mutane 32,684 da suka yi rajista a jihar Legas sun karbi katin zabe na dindindin (PVCs).

 

 

Hukumar  a cikin bayanan ta na yau da kullun kan karbar PVCs da ta fitar ranar Asabar a Abuja, babban birnin ta bayyana  cewa 15,286 daga cikin wadanda suka yi rajistar zabe a Legas da suka karbi PVC mata ne yayin da 17,398 maza ne.

 

 

Hukumar ta kuma bayyana cewa mutane 13,703 da suka yi rajista sun karbi katin zabe su a jihar Edo.

 

 

Karanta kuma: 2023: INEC Za Ta Fara bada Katin zaben ( PVC ) a unguwanni.

 

 

INEC ta mayar da aikin ne a duk fadin kasar nan, na kabar katin zabe a matakin rajista daga ranar 6 ga watan Janairu zuwa 15 ga watan Janairu, daga nan kuma za a mayar da shi ofisoshin kananan hukumomin ta har zuwa ranar 22 ga watan Janairu.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *