Take a fresh look at your lifestyle.

Anji Karar Fashewar Bututun Danyen Mai Da Ya Haifar Da Mutuwar Mutane Da Dama A Koguna

0 173

Mutane da dama ne aka tabbatar da mutuwarsu bayan wani kazamin fashewar danyen mai a yankin Rumuekpe da ke karamar hukumar Emuoha a jihar Ribas a kudancin Najeriya.

 

Lamarin da ya faru da sanyin safiyar Juma’a ana kyautata zaton masu sana’ar tace danyen mai da aka sata ba bisa ka’ida ba da ke aiki a bututun Neja Delta a yankin.

Fashewar ta yi sanadiyyar asarar dukiyoyi na miliyoyin Naira.

 

A halin da ake ciki, mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan jihar Ribas, Grace Iringe-Koko, ta tabbatar da faruwar lamarin, inda ta ce tuni jami’in ‘yan sandan shiyya na kan gaba a lamarin.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *