Take a fresh look at your lifestyle.

Sanwo-Olu Ya Share Kananan Hukumomi 18 Cikin 20 Na Jihar Legas

0 247

Gwamnan jihar Legas kuma dan takarar jam’iyyar All Progressives Congress, Mista Babajide Sanwo-Olu ya lashe kananan hukumomi 18 daga cikin kananan hukumomin jihar 20 a zaben gwamnoni da na ‘yan majalisar dokoki da aka kammala.

Hukumar zabe mai zaman kanta ta sanar da sakamakon zaben a ranar Lahadi a cibiyar tattara sakamakon zaben jihar da ke Yaba, Legas.

Sakamakon zaben dai ya rage daga karamar hukumar Eti-Osa wanda har yanzu ba a fitar da shi ba saboda zaben da ake yi a yanzu haka a rumfar zabe ta Victoria Garden City.

Sanwo-Olu wanda ke neman tazarce ya fafata ne da dan takarar jam’iyyar Peoples Democratic Party, Olajide Oladiran, da dan takarar jam’iyyar Labour, Gbadebo Rhodes-Vivour.

Gwamna mai ci ya samu kuri’u mafi yawa a tsibirin Legas, Epe, Agege, Ibeju-lekki, Surulere, Ikeja, Mushin, Ajeromi-Ifelodun, Apapa, Ifako-Ijaiye, Badagry da Legas Mainland.

Sauran kananan hukumomin da Sanwo-Olu yake sun hada da Alimosho, Ojo, Ikorodu, Kosofe, Oshodi-Isolo, da Amuwo-Odofin.

Sai dai abokin hamayyarsa, Rhodes-Vivour, ya doke jam’iyya mai mulki a Amuwo-Odofin.   Cikakkun bayanai nan ba da jimawa ba…

 

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *