Take a fresh look at your lifestyle.

Dan Takarar Shugabanci A APC Ya Kada Kuri’ar Shi

0 165

Dan takarar shugabancin Najeriya na Jam’iyyar APC Bola Ahmed Tinubu ya kaɗa ƙuri’a a mazaɓar shi ta Awolowo da ke Falomo a Jihar Legas.

 

 

Da misalin ƙarfe 9:30 na safe ne dan takarar ya isa inda zai ƙaɗa kuri’ar tasa tare da mai ɗakinsa Oluremi Tinubu.

An samu jinkiri gabanin fara kaɗa ƙuri’a a rumfar zaɓen, sai dai daga baya zaɓen ya kankama. Akwai mutum aƙalla 832 da suka yi rajistarsu a wannan rumfar zaɓe.

 

 

Yayin da harkokin zaɓe ke ci gaba da gudana a wasu sassan Najeriya lami lafiya, wasu ɓangarorin suna fama da matsaloli da dama.

Kama daga rashin isar jami’an INEC a kan lokaci zuwa na rashin tsaro kamar a abin da ya faru a jihar Gombe.

A Jihar Maidugurin kuma akwai matsalar na’urarar tantance masu kaɗa ƙuri’a ita ce ta ƙi aiki yadda ya kamata.

Kazalika ana fuskantar rashin fitowar masu zaɓe a jihar.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *